Fajirsa Blog

TATTAUNA ALAMURAN DASUKA SHAFI ADDINI, LABARAI, NISHADI, SADA ZUMUNTA

Sunday, January 14, 2018

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI (3)



Dr Saleh Kaura :

2 - Hukuncin idan matar da aka ari mahaifarta ta zamo kishiyar mai kwayoyin halitta:

Mun bayyana cewa malaman Shari’ar Musulunci sun hadu akan haramci bayar da hayar mahaifa, idan mai mahaifar ba ta da dangantaka ta aure da namijin da aka hada maniyyin sa da kwayoyin halittar da aka ciro daga maniyyin matarsa.. Haka ma haramun ne a hada maniyyin namiji da kwayoyin halittar wata macen da ba matarsa ba; domin a shigar a cikin mahaifar matarsa..

Amma idan matar da za ta bayar da mahaifar tata kishiya ce ta mai kwayoyin halittar, ma’ana: matan mutum daya ne, mijinsu daya, to a nan malamai sun yi sabani; wasu suna ganin babu laifi a yi hakan saboda lalura, ganin cewa dukansu matan mutum daya ne. Wasu malaman kuma suna ganin cewa hakan haramun ne, domin ba shi da wani bambanci da surar farko da muka bayyana..

“al-Majma’ul Fiqhiy al-Islamiy”: wato Kungiyar masana ilimin Fiqhun Musulunci sun zartar da hukuncin halaccin irin wannan hali a taro mai lamba 7, da aka yi a Makka, a ranakun : 11 zuwa ranar 16 ga watan Rabi’ul Akhir, shekara 1404 bayana hijirar Sayyiduna RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam).

Sun kuma nuna cewa: tun da duka matan mutum daya ne, kuma ta yiwu kishiyar ce ta bayar da mahaifar tata kyauta, kuma dan da za a haifa a nan dan mutum daya ne, saboda haka babu maganar cakudewar tsatso da dangi..

Koda dai ita kanta wannan kungiya, ta janye wannan fatawar a wani taro mai lamba 8, da aka yi a cibiyar kungiyar “Rabidatul aalamil Islamiy, da take Makka, a ranakun : 28 ga watan Rabi’ul Akhir, zuwa ranar 7 ga watan Jimadal Ula, shekara 1405 bayana hijirar Sayyiduna RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam), wanda ya zo daidai da 19 – 28, ga watan Junairu, 1985, inda suka bayar da fatawar haramcin wannan sura da mai bayar da mahaifar za ta zamo kishiyar mai kwayoyin halitta.

FATAWAR DA TAFI KARFI:

Babu shakka, fatawar haramcin ita ce ta fi karfi; saboda babu wani dalili mai karfi da zai sanya a kebance wannan sura akan ta farko, musamman idan mun kalli hujjojin da idon basira.

******

Idan hakan ya riga ya faru –duk da cewa haramun ne-, har ya kai ga an sami da, an kuma haife shi, to babu shakka akwai bukatar sanin hakikanin uwa da uban wannan jariri, da wane za a danganta shi? Domin akwai hakkokinsa tun daga tarbiyya har zuwa gado, su ma iyayen suna da nasu hakkokin na zamansu iyaye; saboda haka insha Allah wannan babin za mu tabo a bayani na gaba.

Was Salamu alaikum.



© TASKAR SUNNA

No comments:

Post a Comment